6. Za a kai ɗan maraƙin a AssuriyaDon a biya wa sarki haraji.Za a kunyatar da Ifraimu,Isra'ila kuwa za ta ji kunya saboda shawararta.
7. Sarakunan Samariya za su ɓace,Kamar kumfa a bisa ruwa.
8. Za a hallaka masujadan tuddai na Awen inda Isra'ila suke yin zunubi,Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma a bagadansu.Za su ce wa manyan duwatsu, “Ku rufe mu!”Su ce wa tuddai, “Ku faɗo bisa kanmu!”
9. Ubangiji ya ce, “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra'ila!Tun daga wancan lokaci kuka yi ta ci gaba.Ashe, yaƙi ba zai tarshe su a Gibeya ba?