13. Kun shuka mugunta,Kun girbe rashin adalci,Kun ci amfanin ƙarya.“Da yake dogara ga hanyarku da ɗumbun sojojinku,
14. Domin haka hayaniyar yaƙi za ta tashi a tsakanin jama'arku.Dukan kagaranku za a hallaka su.Kamar yadda Shalmanesar ya hallaka Bet-arbel a ranar yaƙi.An fyaɗa uwaye da 'ya'yansu a ƙasa.
15. Haka za a yi muku, ya mutanen Betel, saboda yawan muguntarku.Da asuba za a datse Sarkin Isra'ila.”