Yah 6:59-61 Littafi Mai Tsarki (HAU)

59. Wannan kuwa a majami'a ya faɗa, sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.

60. Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan magana mai wuya ce, wa zai iya jinta?”

61. Yesu kuwa, da yake ya sani a ransa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce musu, “Wato, wannan ne ya zamar muku abin tuntuɓe?

Yah 6