16. Da magariba ta yi, sai almajiransa suka gangara teku.
17. Suka shiga jirgi suka tasar wa haye tekun zuwa Kafarnahun. A sa'an nan duhu ya yi, Yesu kuwa bai zo wurinsu ba tukuna.
18. Sai tekun ta fara hauka saboda wata riƙaƙƙiyar iska da take busowa.
19. Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko huɗu, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan ruwan, ya kusato jirgin. Sai suka firgita.