33. Dā kam, ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa, shi ne ya ce mini, ‘Wanda ka ga Ruhun na sauko masa, yana kuma kasance a kansa, shi ne mai yin baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34. Na kuwa gani, na kuma yi shaida, cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35. Kashegari kuma Yahaya na tsaye da almajiransa biyu.
36. Yana duban Yesu na tafiya, sai ya ce, “Kun ga, ga Ɗan Rago na Allah!”