9. Duk lokaci kuma da rayayyun halittan nan suka ɗaukaka wanda yake zaune a kan kursiyin, yake kuma raye har abada abadin, suka girmama shi, suka kuma gode masa,
10. sai dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi a gaban wanda yake a zaune a kan kursiyin, su yi masa sujada, shi da yake a raye har abada abadin, su kuma ajiye kambinsu a gaban kursiyin, suna waƙa, suna cewa,
11. “Macancanci ne kai, ya Ubangiji Allahnmu,Kă sami ɗaukaka, da girma, da iko,Domin kai ne ka halicci dukkan abubuwa,Da nufinka ne suka kasance aka kuma halicce su.”