1. Bayan wannan na ji kamar wata sowa mai ƙarfi ta ƙasaitaccen taro a Sama, suna cewa,“Halleluya! Yin ceto, da ɗaukaka, da iko, sun tabbata ga Allahnmu,
2. Don hukuncinsa daidai yake, na adalci ne,Ya hukunta babbar karuwar nan wadda ta ɓata duniya da fasikancinta,Ya kuma ɗauki fansar jinin bayinsa a kanta.”