23. To, “lasafta masa” ɗin nan da aka rubuta kuwa, ba saboda Ibrahim kaɗai aka rubuta ba,
24. har saboda mu ma, za a lasafta mana, wato mu da muke gaskatawa da wannan da ya ta da Yesu Ubangijinmu daga matattu,
25. wanda aka bayar a kashe saboda laifofinmu, aka kuma tashe shi, domin mu sami kuɓuta ga Allah.