Mat 27:12-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. Amma da manyan firistoci da shugabanni suka kai ƙararrakinsa, bai ce kome ba.

13. Sai Bilatus ya ce masa, “Ba ka ji yawan maganganun da suke ba da shaida a kanka ba?”

14. Amma bai ba shi wata amsa, ko da ta kalma ɗaya ba, har mai mulki ya yi mamaki ƙwarai.

15. To, a lokacin idi kuwa mai mulki ya saba sakar wa jama'a kowane ɗaurarre guda da suka so.

Mat 27