Mat 15:15-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Amma Bitrus ya ce masa, “A yi mana fassarar misalin nan.”

16. Yesu ya ce, “Ku ma, ashe, har yanzu ba ku fahimta?

17. Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum ta baka, cikinsa ya shiga, ta haka kuma zai fice?

18. Amma abin da ya fito ta baka, daga zuci yake, shi ne kuwa yake ƙazantar da mutum.

19. Don daga zuci mugayen tunani suke fitowa, kamar su kisankai, da zina, da fasikanci, da sata, da shaidar zur, da yanke.

20. Waɗannan suke ƙazantar da mutum. Amma a ci da hannu marar wanki ba ya ƙazantar da mutum.”

21. Yesu ya tashi daga nan, ya tafi zuwa ƙasar Taya da Sidon.

Mat 15