16. Sai ya kwaɓe su, kada su bayyana shi.
17. Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa,
18. “Ga barana wanda na zaɓa!Ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai.Zan sa masa Ruhuna, zai kuma sanar da al'ummai hanyar gaskiya.
19. Ba zai yi husuma ko magana sama sama ba,Ba kuma wanda zai ji muryarsa tasa a titi.
20. Kyauron da ya tanƙwasa ba zai kakkarye shi ba,Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai kashe ta ba,Har ya sa gaskiya ta ci nasara.
21. Al'ummai kuma za su sa zuciya ga sunansa.”
22. Sai aka kawo masa wani beben makaho mai aljan, ya kuwa warkar da shi, har beben ya yi magana, ya kuma gani.
23. Mutane duk suka yi al'ajabi, suka ce, “Shin, ko wannan shi ne Ɗan Dawuda?”