Mar 2:3-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Sai suka kawo masa wani shanyayye, mutum huɗu suna ɗauke da shi.

4. Da suka kāsa kusatarsa don yawan mutane, suka buɗe rufin soron ta sama da shi. Da suka huda ƙofa kuwa, suka zura gadon da shanyayye yake kwance a kai.

5. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, an gafarta maka zunubanka.”

6. To, waɗansu malaman Attaura na nan zaune, suna ta wuswasi a zuciya tasu,

Mar 2