9. Sai mun yi kasai da ranmu kafin mu sami abinci,Domin akwai masu kisa a jeji.
10. Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu,Saboda tsananin yunwa.
11. An yi wa mata faɗe a cikin Sihiyona,Haka kuma aka yi wa budurwai a garuruwan Yahuza.
12. An rataye shugabanni da hannuwansu,Ba a kuma girmama dattawa ba.
13. An tilasta wa samari su yi niƙa,Yara kuma suna tagataga da kayan itace.