M. Sh 33:6-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. “Allah ya sa Ra'ubainu ya rayu, kada ya mutu,Kada mutanensa su zama kaɗan.”

7. A kan Yahuza ya ce,“Ka ji muryar Yahuza, ya Ubangiji,Ka kawo shi wurin jama'arsa.Ka yi yaƙi da ikonka dominsu,Ka taimake shi a kan maƙiyansa.”

8. A kan Lawi ya ce,“Ka ba Mai Tsarki Tumminka da Urim naka,Shi wanda ka jarraba a Masaha,Wanda ka yi jayayya da shi a ruwan Meriba,

M. Sh 33