18. Kun ƙi kula da Dutsen da ya haife ku,Kun manta da Allahn da ya ba ku rai.
19. “Ubangiji ya gani, ya raina su,Saboda tsokanar da 'ya'yansa mata da maza suka yi masa.
20. Ya ce, ‘Zan ɓoye musu fuskata,Zan ga yadda ƙarshensu zai zama.Gama su muguwar tsara ce,'Ya'ya ne marasa aminci.