1. “Ku saurara, ya ku sammai, gama zan yi magana,Bari duniya ta ji maganar bakina.
2. Bari koyarwata ta zubo kamar ruwan sama,Maganata ta faɗo kamar raɓa,Kamar yayyafi a bisa ɗanyar ciyawa,Kamar ɗiɗɗigar ruwa a bisa ganyaye.
3. Gama zan yi shelar sunan Ubangiji,In yabi girman Allahnmu!