M. Sh 24:9-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Maryamu a lokacin da kuka fito daga Masar.

10. “Idan kun ba maƙwabcinku rance na kowane iri, kada ku shiga gidansa don ku ɗauki jingina.

11. Sai ku tsaya a waje, mutumin da kuka ba shi rancen zai kawo muku jinginar.

12. Amma kada ku yarda abin da aka jinginar ya kwana a wurinku idan mutumin matalauci ne.

13. Sai ku mayar masa da shi a faɗuwar rana domin ya yi barci yafe da rigarsa ya gode muku. Yin haka zai zama muku adalci a wurin Ubangiji Allahnku.

M. Sh 24