Luk 3:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Sai taron suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi ke nan?”

11. Ya amsa musu ya ce, “Duk mai taguwa biyu, ya raba da marar ita, mai abinci ma haka.”

12. Masu karɓar haraji ma suka zo a yi musu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?”

13. Ya ce musu, “Kada ku karɓi fiye da abin da aka umarce ku.”

14. Waɗansu soja ma suka tambaye shi, “To, mu fa, me za mu yi?” Sai ya ce musu, “Kada ku yi wa kowa ƙwace ko ƙazafi. Ku dai dangana da albashinku.”

Luk 3