L. Kid 32:10-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Saboda haka Ubangiji ya husata a ranan nan, har ya yi wa'adi ya ce,

11. ‘Hakika ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, domin ba su bi ni sosai ba.

12. Sai dai Kalibu, ɗan Yefunne Bakenizze, da Joshuwa ɗan Nun, domin su ne kaɗai suka bi ni sosai.’

L. Kid 32