15. Ya tambaye su ya ce, “Don me kuka bar dukan mata da rai?
16. Ku tuna fa, su ne, ta wurin shawarar Bal'amu, suka yaudari Isra'ilawa, suka saɓi Ubangiji cikin maƙidar Feyor, har annoba ta fasu a jama'ar Ubangiji.
17. Yanzu, sai ku kashe dukan yara maza da kowace mace wadda ta san namiji.
18. Amma dukan 'yan mata da ba su san maza ba, sai ku bar wa kanku.