L. Kid 14:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai dukan taron jama'a suka yi kuka da babbar murya dukan dare saboda wahala.

2. Dukan Isra'ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, suke ce, “Da ma mun mutu a ƙasar Masar, ko kuwa a wannan jeji.

3. Me ya sa Ubangiji ya kawo mu a wannan ƙasa, mu mutu da takobi? Matanmu da ƙanananmu za su zama ganima. Ba zai fi mana kyau, mu koma Masar ba?”

L. Kid 14