L. Fir 23:23-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa,

24. ya ce wa Isra'ilawa su mai da rana ta fari ga wata na bakwai ta zama ranar hutu musamman, sa'ad da za su ji busar ƙaho, sai su taru domin yin sujada.

25. Ba za su yi aiki mai wuya ba. Za su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.

26. Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa,

27. rana ta goma ga watan bakwai za ta zama rana ta yin kafara da lokacin yin muhimmin taro. Kada su ci abinci a ranar, su taru su yi sujada, su miƙa hadaya taƙonawa ga Ubangiji.

L. Fir 23