18. Muddin matarsa tana da rai, ba zai auro ƙanwarta ta zama kishiyarta ba.
19. Kada ya kwana da mace a lokacin hailarta, gama ba ta da tsarki.
20. Kada ya kwana da matar maƙwabcinsa don kada ya ƙazantar da kansa.
21. Kada ya ba da ɗaya daga cikin 'ya'yansa don a miƙa wa Molek, gama yin haka zai ƙasƙantar da sunan Allah. Shi Ubangiji ne.
22. Kada ya yi luɗu, gama Allah yana ƙin wannan.