Dan 7:2-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Daniyel ya ce, “A wahayi da dare na ga iskar samaniya daga kusurwa huɗu tana gurɓata babbar teku.

3. Sai manyan dabbobi huɗu iri dabam dabam suka fito daga cikin tekun.

4. Kamannin dabba ta fari irin ta zaki ce, amma tana da fikafikan gaggafa. Ina kallo, sai aka fige fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.

Dan 7