Dan 4:9-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. ‘Ya Belteshazzar shugaban masu sihiri, tun da yake na san ruhun alloli tsarkaka yana a cikinka, ba wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga mafarkin da na yi, sai ka faɗa mini fassararsa.

10. “ ‘Wahayin da na gani ke nan sa'ad da nake kwance a gadona. Na ga wani itace mai tsayi ƙwarai a tsakiyar duniya.

11. Itacen ya yi girma, ya ƙasaita,Ƙwanƙolinsa ya kai har sama,Ana iya ganinsa ko'ina a duniya.

12. Yana da ganyaye masu kyauDa 'ya'ya jingim don kowa da kowa ya ci.Namomin jeji suka sami inuwa a ƙarƙashinsa,Tsuntsayen sama kuma suka zauna a rassansa.Dukan masu rai a gare shi suka sami abinci.

13. “ ‘A cikin wahayin da na gani sa'ad da nake kwance a gado, sai ga wani mai tsaro, tsattsarka, ya sauko daga sama.

14. Sai ya yi magana da ƙarfi, ya ce,“A sare itacen, a daddatse rassansa,A zage ganyayensa ƙaƙaf, a warwatsar da 'ya'yansa.A sa namomin jeji su gudu daga ƙarƙashinsa,Tsuntsaye kuma su tashi daga rassansa.

15. Amma a bar kututturen da saiwoyinsa a ƙasaƊaure da sarƙar baƙin ƙarfe da tagulla.A bar shi can cikin ɗanyar ciyawar saura,Ya jiƙe da raɓa,Ya yi ta cin ciyawa tare da namomin jeji.

Dan 4