12. Saboda haka sarki ya husata ƙwarai, ya umarta a karkashe duk masu hikima na Babila.
13. Sai doka ta fita cewa a karkashe masu hikima. Aka nemi Daniyel da abokansa don a kashe su.
14. Daniyel kuwa ya amsa wa Ariyok, shugaban dogaran sarki, a hankali da hikima, sa'ad da Ariyok ya fita don ya karkashe masu hikima na Babila.
15. Daniyel ya ce wa Ariyok shugaban dogaran sarki, “Me ya sa ake gaggauta dokar sarki haka?” Sai Ariyok ya bayyana wa Daniyel yadda al'amarin yake.
16. Sa'an nan Daniyel ya shiga wurin sarki, ya roƙe shi ya ba shi lokaci domin ya yi masa fassarar.