4. A ina kake sa'ad da na aza harsashin gina duniya?Faɗa mini idan ka sani.
5. Wane ne ya zayyana kusurwoyinta?Hakika ka sani.Wane ne kuma ya auna ta?
6. A kan me aka kafa tushenta?Wa ya aza dutsen kan kusurwarta?
7. Sa'ad da taurarin asuba suka raira waƙa tare,Sai mala'iku duka suka yi sowa saboda murna.