20. A iya faɗa masa, cewa zan yi magana?Mutum ya taɓa so a haɗiye shi da rai?
21. “A yanzu dai mutane ba su iya duban haske,Sa'ad da yake haskakawa a sararin sama,Bayan da iska ta hura ta share gizagizai sarai.
22. Daga arewa wani haske kamar na zinariya ya fito mai banmamaki,Allah yana saye da ɗaukaka mai bantsoro.
23. Mai Iko Dukka, ya fi ƙarfin ganewarmu,Shi mai girma ne, da iko, da gaskiya,Da yalwataccen adalci,Ba ya garari.