Ayu 30:20-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. “Na yi kira gare ka, ya Allah, amma ba ka amsa mini ba,Na yi addu'a kuma, amma ba ka kula da ni ba.

21. Ka zama mugu a gare ni,Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini.

22. Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ni in hau ta,Ka yi ta shillo da ni cikin rugugin hadiri.

Ayu 30