Amos 5:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ku kasa kunne, ku jama'arIsra'ila, ga waƙar makoki da zan yia kanku.

2. Isra'ila ta fāɗi,Ba kuwa za ta ƙara tashi ba.Tana fa kwance a ƙasa,Ba wanda zai tashe ta.

3. Ubangiji ya ce,“Wani birnin Isra'ila ya aika da sojadubu,Ɗari ne kaɗai suka komo,Wani birni kuma ya aika da soja ɗarine,Amma goma kaɗai suka komo.”

4. Ubangiji ya ce wa jama'ar Isra'ila,“Ku zo gare ni, za ku tsira.

Amos 5