A.m. 2:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Wannan, ai, shi ne abin da Annabi Yowel ya faɗa cewa,

17. ‘Allah ya ce,A zamanin karshe zai zamanto zan zubo wa dukan 'yan adam Ruhuna.'Ya'yanku mata da maza za su yi annabci,Wahayi zai zo wa samarinku,Dattawanku kuma za su yi mafarkai.

18. Hakika, har ma a kwanakin nan zan zubo Ruhuna a kan bayina mata da maza,Za su kuma yi annabci.

19. Zan nuna abubuwan al'ajabi a sararin sama,Da mu'ujizai a nan ƙasa,Wato jini, da wuta, da kuma, hauhawan hayaƙi.

20. Za a mai da rana duhu,Wata kuma jini,Kafin Ranar Ubangiji ta zo,Babbar ranar nan mai girma.

A.m. 2