Afi 5:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Don haka kada ku zama marasa azanci, sai dai ku fahimci abin da yake nufin Ubangiji.

18. Kada kuma ku bugu da giya, hanyar masha'a ke nan. Sai dai ku cika da Ruhu,

19. kuna zance da junanku da kalmomin zabura, da waƙoƙin yabo, da waƙoƙi na ruhu, kuna raira waƙoƙi da zabura ga Ubangiji da yabo a zukatanku.

20. Kullum ku riƙa gode wa Allah Uba da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a kan ko mene ne.

Afi 5