10. Ku dai tabbata abin zai gamshi Ubangiji.
11. Ku yi nesa da ayyukan duhu na banza da wofi, sai dai ku tona su.
12. Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da suke yi a asirce.
13. Duk abin da aka kawo a gaban haske a san ainihinsa, gama duk abin da aka san ainihinsa ya haskaka.
14. Saboda haka aka ce,“Farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu.Almasihu kuwa zai haskaka ka.”