1 Tas 5:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Amma da yake mu na rana ne, sai mu natsu, muna saye da sulken bangaskiya da ƙauna, muna begen samun ceto, shi ne kuma kwalkwakinmu.

9. Allah bai ƙaddara mu ga fushinsa ba, sai dai ga samun ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu,

10. wanda ya mutu saboda mu, domin ko muna a raye, ko muna barci, mu zama muna tare da shi.

11. Saboda haka, sai ku ƙarfafa wa juna zuciya, kuna riƙa inganta juna, kamar dai yadda kuke yi.

1 Tas 5