1 Tar 21:18-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Mala'ikan Ubangiji ya umarci Gad ya faɗa wa Dawuda ya haura, ya gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna Bayebuse.

19. Dawuda kuwa ya haura kamar yadda Gad ya faɗa masa da sunan Ubangiji.

20. Arauna yana cikin sussukar alkama, sai ya waiwaya ya ga mala'ika. 'Ya'yansa maza su huɗu kuwa, waɗanda suke tare da shi suka ɓuya.

21. Sa'ad da Dawuda ya tafi wurin Arauna, da Arauna ya ga Dawuda, sai ya fito daga masussukar ya tafi ya fāɗi rub da ciki a gaban Dawuda ya gaishe shi.

22. Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ba ni wannan masussuka don in gina wa Ubangiji bagade. Ka sayar mini da masussukar a bakin cikakken kuɗinta, domin a kawar wa jama'a da annobar.”

1 Tar 21