1 Kor 10:6-12 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. To, ai, waɗannan abubuwa gargaɗi ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi.

7. Kada fa ku zama matsafa kamar yadda waɗansunsu suke. A rubuce yake cewa, “Jama'a sun zauna garin ci da sha, suka kuma tashi suka yi ta rawa.”

8. Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har mutum dubu ashirin da uku suka zuba a rana ɗaya tak.

9. Kada kuma mu gwada Ubangiji yadda waɗansu suka yi, har macizai suka hallaka su.

10. Kada kuma mu yi gunaguni yadda waɗansu suka yi, har mai hallakarwa ya hallaka su.

11. To, duk wannan ya same su ne a kan misali, an kuma rubuta shi ne don a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana.

12. Don haka duk wanda yake tsammani ya kahu, ya mai da hankali kada ya fāɗi.

1 Kor 10